An shawarci samarin mazabar *Dalijan* akan su cigaba da marawa gwamnatin karamar hukumar *Gwandu* baya karkashin jagorancin *Hon. Shehu Bagudu Dalijan*.


PRESS RELEASE 1:
Wednesday, 21/02/2018

An shawarci samarin mazabar *Dalijan* akan su cigaba da marawa gwamnatin karamar hukumar *Gwandu* baya karkashin jagorancin *Hon. Shehu Bagudu Dalijan*.


*Hon. Usman Buhari Ali Gwandu (Shettiman Garin Gwandu)* ya bada shawarar lokacin da *Kungiyar Matasan Solar, Dalijan* karkashin jagorancin *Abdullahi Sani (280)* suka gayyaceshi domin ganin aiyukan gayya da sukeyi domin cigaban garin.

*Shettiman Garin Gwandu* ya kara da cewa karamar hukumar Gwandu tana kokarinta wurin kawo cigaba a karamar hukumar, a inda yanzu haka an tura mutane shida (6) domin koyon gyaran rijiyar burtsatse.

*Hon. Shehu Dalijan* ya tabbatar da cewa yanzu haka ma'aikatan sun fara da gyaran rijiyoyi uku (3), biyu (2) a *Kurya* da guda daya (1) a cikin *sakatariyar karamar hukumar Gwandu*, sannan an kayyade gyaran guda ashirin (20) a mazabai guda (10) cikin karamar hukumar.

Bayan zagayen dubin aiyukan gyaran hanya tare da *Hon. Usman Buhari* da matasan kungiyar sukayi ta *Hanyar Sabon Gari* da *Hanyar Kasuwa*, sun kara da cewa zasu cigaba da aikin gyaran hanya a garkar *Malam Abdullahi Liman* da aikin gyaran gidan almajirai su kimanin guda dari (100) da ke gidan *Malam Liman Yahaya*

Samarin sun kara jinjinarsu da goyon bayan gwamnati da tabbatar da cewa babu cin zarafi cikin tafiyarsu.

Shugaban matasan jam'iyar APC ta *mazabar Dalijan*, *Malam Umar Idde* shi Ma ya yi bayanai akan manufofin *Hon. Usman Buhari* musamman ta fannin kokarin matasa sun samu abun yi a hannu.

A karshe *Hon Usman Buhari* a madadin kansa da shugaban karamar mulkin *Gwandu Hon. Shehu Bagudu Dalijan* sun bada gudun mawar naira dubun ashirin (N20,000) ga matasan domin cigaba da ayyukansu.

*Hon. Usman Buhari* kuma ya ziyarci wani matashi a garin *Dalijan* da yayi hatsari ya karye. Allah Ya kara masa lafiya

Media Support Team
*Shettima Foundation Gwandu*

Comments