A yammacin yau ne *Hon. Usman Buhari Ali Gwandu (Shettiman Garin Gwandu)* ya kai ziyara babban asibitin
PRESS RELEASE2:
Sunday,
18/02/2018
A yammacin
yau ne *Hon. Usman Buhari Ali Gwandu (Shettiman Garin Gwandu)* ya kai ziyara
babban asibitin *Mazabar Kambaza* wurin dubin *Hajiya Muna Kambaza Mai Tuwo*
mai kimanin shekaru 85 da aka kwantar. Ya yi amfani da wannan dama domin duba
sauran majinyata kuma Ya roki Allah akan Ya basu lafiya.
*Hon. Usman
Buhari* ya kuma samu tattauna nasarorin gwamnati da wasu dattijai da matasan
garin *Kambaza*. Sun kuma nuna bukatar gwamnati da ta cigaba da waiwayo
jiga-jigan yan siyasa da suka wahala domin kara saukin cin nasarar zabe mai
zuwa.
*Shettiman
Garin Gwandu* kuma ya halarci kwallo zagayen karshe wanda *Young Soccer
Committee* suka hada a garin Gwandu, wadda ita ce ta karshe tsakanin yan wasan
*Young Pillars* ta yi nasara akan *Junior Fulham* da 1-0.
An bada
kyaututtuka da dama kuma *Hon. Usman Buhari* ya dauki nauyin daurin karayar
wani dan wasa mai suna *Dawuda* da ya karye a kafa cikin wasa.
Media
Support Team
*Shettima
Foundation Gwandu*

Comments
Post a Comment